Badakalar Kudade: Hukumar EFCC Ta Tsare Dan Takarar Gwamnan Jihar Ondo
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
Jihar Ondo - Hukumar yaƙi da yi wa tattalin arziƙin ƙasa ta’annati (EFCC) ta tsare wani ɗan takarar gwamna na zaɓen fidda gwanin jam’iyyar APC a jihar Ondo, Wale Akinterinwa.
Akinterinwa dai yana hannun hukumar EFCC ne a bisa binciken da ake yi kansa na kujerar kwamishinan kuɗi da ya riƙe na shekara bakwai a lokacin mulkin tsohon gwamna Rotimi Akeredolu.
Jaridar The Nation ta ce wani majiya da ya zanta da manema labarai kan lamarin ya bayyana cewa ana binciken tsohon kwamishinan ne bisa zargin almundahanar biliyoyin Naira.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Hukumar EFCC ta gayyaci Akinterinwa a makonnin da suka gabata domin tattaunawa kan wasu zarge-zarge amma bai mutunta gayyatar ba sai ranar Alhamis, 18 ga watan Afrilun 2024, cewar rahoton Politics Nigeria.
A cewar majiyar:
"A makonnin da suka gabata, EFCC ta gayyaci Akinterinwa domin yi masa tambayoyi kan wasu batutuwa a lokacin da yake kwamishinan kuɗi. Amma bai amsa gayyatar ba."
"Hukumar nada zaɓin bayyana a matsayin wanda ake nema ruwa a jallo, amma ta haƙura saboda kada siyasa ta shigo ciki domin yana takarar gwamna a zaɓen fidda gwanin jam'iyyar APC."
"Amma Akinterinwa ya kawo kansa ga hukumar EFCC a Abuja. An tsare shi domin yi masa tambayoyi."
“Akinterinwa yana tsare a hannunmu. Ba mu kamo shi ba, shi ne ya kawo kansa bisa gayyatar da muka yi masa tun kwanaki. Ina baka tabbaci cewa tsare shi baya da alaƙa da siyasa."
A wani labarin kuma, kun ji cewa hukumar EFCC ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin wanda ake nema ruwa a jallo.
Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawan na neman Yahaya Bello ne bisa laifukan da suka shafi almundahanar maƙudan kuɗaɗe
Asali: Legit.ng