Cin Zarafin Naira: EFCC Ta Kama Matashi Saboda Likin Kudi a Gidan Rawa
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Jihar Gombe - Hukuma mai yaki da yiwa tattalin kasa zagon kasa (EFCC) ta sanar da kama wani matashi a jihar Gombe bisa zargin cin zarafin Naira.
A yau Laraba ne hukumar EFCC ta wallafa labarin a shafinta na X inda ta ce jami'anta a jihar Gombe sun kama matashin.
Matashin mai suna Zachariyya Muhammad ya masa laifinsa yayin da hukumar ta ke masa tambayoyi.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Hukumar EFCC ta bayyana cewa ta samu bidiyon matashin ne yana rawa yana manna kudi 'yan N200 a wani gidan rawa da ke Tufure a jihar Gombe.
Bayan tsananta bincike hukumar ta samo matashin, bayan ta nuna masa bidiyon ya tabbatar da cewa shi ne ya aikata laifin.
Hukumar ta ce a halin yanzu za ta mika Zachariyya Muhammad gaban kotu domin Alkali ya bincikesa da kuma yanke masa hukuncin da ya dace.
Kama Zachariyya Muhammad ya biyo bayan kama shahararrun mutane da hukumar ta yi a kwanan nan domin yaki da cin zarafi Naira.
A wani rahoton, kun ji cewa gamayyar kungiyoyin fararen hula karkashin kungiyar NCSO sun nemi hukumar EFCC da ta kama tare da hukunta Monday Okpebolo.
Rahotanni sun nuna cewa kungiyar NCSO, ta zargi Okpebolo, wanda shi ne dan takarar gwamnan jihar Edo da cin zarafin Naira a wani taron biki.
An ce cin zarafin Naira ya sabawa dokar babban bankin Najeriya (CBN) ta 2007 wanda ka iya kaiwa ga daure mutum wata shida a gidan gyaran hali.
Asali: Legit.ng