Jagororin EU sun amince da kara wa von der Leyen wa'adi
Jagororin kungiyar tarayyar Turai EU sun amince da kara wa Ursula von der Leyen wa'adin mulkin shugabancin kungiyar a hukumance, a taron da suka gudanar a Brussels, kamar yadda shugaban majalisar kungiyar Charles Michel ya tabbatar a shafinsa na X.
Bisa yarjejeniyar da jagororin suka cimma yayin taron, sun amince da nadin tsohon firaministan Portugal Antonio Costa a matsayin sabon shugaban majalisar dokokin EU, sai kuma firaministan Estonia Kaja Kallas da zai karbi mukamin babban jami'in diflomasiyyar kungiyar.
Wani sako da firaministan Poland Donald Tusk ya wallafa a shafinsa na X, ya tabbatar da cewa wadanda aka bai wa sabbin mukaman sun amince su karba.