Home Back

Katsina: Gwamna Ya Ba Ma’aikata Goron Sallah N45,000, Ya Gindaya Sharuda

legit.ng 2024/7/7
  • Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda ya ba ma’aikatan jihar kyautar N15,000 da bashin N30,000 domin bikin sallah
  • Gwamnan ya ce ma’aikatan za su biya N30,000 cikin watanni uku da za a fara cirewa daga watan Yuli mai kamawa
  • Wannan matakin gwamnan na zuwa ne yayin ake shirye-shiryen gudanar da bikin babbar salla a fadin duniya baki daya

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Katsina – Gwamna Umaru Dikko Radda na jihar Katsina ya gwangwaje ma’aikata da barka da sallah a jihar.

Radda ya ba da kyautar N15,000 ga duka ma’aikatan jihar yayin da kuma ya ba su bashin N30,000 domin gudanar da salla cikin walwala.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da gwamnan ya wallafa a shafinsa na X a yau Asabar 8 ga watan Yuni.

Gwamnan ya ce ya dauki wannan matakin ne domin ragewa ma’aikatan jihar halin da ake ciki a fadin kasar.

“Ganin yadda babbar sallah ke karatowa, na dauki matakin tallafawa ma’aikata wurin ba su bashin N45,000 hade da goron sallah.”

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

“Domin saukaka musu biyan kudin cikin sauki, za a cire N10,000 kowane wata har N30,000 a watannin Yuli da Agusta da kuma Satumba.”
“Sannan na ba duka ma’aikatan jihar kyautar N15,000 domin gudanar da bukuwan sallah cikin walwala.”

Dikko Umaru Radda

Karin bayani na tafe...

Asali: Legit.ng

People are also reading