Bayan Hana Hawan Sallah, NSCDC Ta Dauki Kwakkwaran Mataki Awanni Kafin Idi a Kano
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Jihar Kano- Hukumar tsaron fararen hula ta NSCDC ta bayyana kammala shirye-shiryen tabbatar da tsaron dukiya da rayukan jama’a a domin gudanar da bikin sallah babba a Kano.
NSCDC ta shaida cewa ta baza jami’anta akalla 3,168 a sassan Kano domin ganin jama’asun bi doka da oda yayin shagulgulan sallah babba, yayin da jihar ke cikin yanayin dambarwar masarauta.
Leadership News ta wallafa cewa jami’in hulda da jama’a na hukumar a Kano, Ibrahim Abdullahi ne ya tabbatar da shirin da su ke yi na tsaron al’umma domin gudanar da shagulgulan sallah lafiya.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Hukumar tsaron fararen hula ta NSCDC ta ce za ta yi aikin hadin gwiwa da sauran jami'an tsaro a Kano yayin bukukuwan sallah babba a loko da sakon jihar. Punch News ta wallafa cewa hukumar za ta yi aiki da hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa a Kano (KAROTA), DSS, FRSC da 'yan sanda wajen wanzar da zaman lafiya a jihar.
Da ya ke zantawa da Legit Hausa ta wayar tarho, kakakin hukumar, Ibrahim Abdullagi ya bayar da tabbacin za su kare dukiya da rayukan jama'a yayin bukukuwan sallah da bayanta.
A baya mun kawo muku labarin cewa wani malamin addinin musulunci Dr. Tajudeen Adebayo ya shawarci musulmi da za su yi layya a sallar bana su tuna da makotansu.
Ya bayyana haka ne yayin da ake zaton matsin rayuwa zai hana musulmin kasar nan da yawa sayen dabbar da za su yi layya da ita, lamarin da malamin ya ce ka da a shiga damuwa da yawa a kai.
Asali: Legit.ng