Tinubu Ya Bi Sahun Atiku Kan Ta'aziyyar Kisan Katsina, Ya Ba Jami'an Tsaro Sabon Umarni
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
FCT, Abuja - Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya yi kakkausar suka kan kashe-kashen da ƴan bindiga suka yi a jihar Katsina.
Ƴan bindigan dai sun kai hare-hare cikin ƴan kwanakin nan a ƙananan hukumomin Dutsinma da Kankara na jihar Katsina.
Ƴan bindigan a yayin hare-haren sun hallaka rayukan mutane da dama waɗanda ba su ji ba, ba su gani ba.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya umarci jami’an tsaro da su zaƙulo ƴan bindigan da suka kai hare-haren a ƙananan hukumomin Dutsinma da Kankara.
Ya kuma umarci su tabbatar da cewa waɗanda suka kai hare-haren an yi musu hukuncin da ya dace.
Shugaban ƙasan ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Ajuri Ngelale ya fitar, wacce Dada Olusegun ya sanya a shafinsa na X.
Shugaba Tinubu wanda ya yi kakkausar suka kan sababbin hare-haren da ake kaiwa a yankunan, ya bayyana su a matsayin waɗanda suka ƙazanta.
Shugaba Tinubu,ya jaddada cewa za a ƙara ƙaimi wajen tabbatar da tsaron ƴan ƙasa da kuma kawo ƙarshen ayyukan ƴan ta’adda gaba ɗaya da sauran masu tayar da ƙayar baya a sassa daban-daban na ƙasar nan.
Ya jajantawa iyalan waɗanda suka rasa rayukansu, gwamnati da al’ummar jihar Katsina, ya kuma yi addu’ar Allah ya jikan waɗanda suka rasu.
A wani labarin kuma, kun ji cewa tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya bayyana takaicin yadda aka mayar da ran ƴan ƙasar nan ba a bakin komai ba.
Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasan wanda ya yi Allah wadai da kisan da ƴan bindiga suka yi a jihar Katsina, ya koka kan yadda ƴan bindiga ke cin karensu babu babbaka.
Asali: Legit.ng