PDP Ta Garzaya Kotu Kan Batun Tsige Shugabanta Na Kasa, Ta Nemi Wata Bukata
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
FCT, Abuja - Jam'iyyar PDP ta ƙalubalanci umarnin babban kotun tarayya na hana ta sauke shugabanta na ƙasa, Umar Damagum.
Damagum wanda ya taɓa zama mataimakin shugaban jam’iyyar PDP na ƙasa (Arewa) ya zama shugaban riƙo na kasa bayan da kotu ta dakatar da shugaban jam’iyyar na ƙasa Iyorchia Ayu.
A kwanakin baya ne dai babbar kotun tarayya ta hana PDP tsige Damagum ko maye gurbinsa har sai ta yi hukunci kan ƙarar da ke gabanta mai lamba FHC/ABJ/CS/579/2024.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
A wata tattaunawa da jaridar Punch, mai baiwa jam’iyyar PDP shawara kan harkokin shari’a, Kamaldeen Ajibade (SAN), ya bayyana cewa jam’iyyar ta shigar da ƙorafin.
Ajibade ya ce jam’iyyar na buƙatar kotu ta yi watsi da shari'ar, inda ya ce lamarin cikin gida ne.
Ya ƙara da cewa a ranar 1 ga watan Yuli ne kotun za ta saurari ƙarar.
"Ba mu buƙatar ɗaukaka ƙara saboda ba a yanke hukunci ba. Abin da suka samu shi ne hukuncin wucin gadi, amma za a saurari ƙarar domin duba cancantar ta a ranar 1 ga watan Yuli."
"Jam’iyyar ta shigar da ƙorafinta. Babban abin da ke a cikin ƙorafin jam’iyyar shi ne, muna roƙon kotu da ta yi watsi da shari’ar domin al’amarin cikin gida ne na jam’iyyar."
- Kamaldeen Ajibade
A wani labarin kuma, kun ji cewa jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ta kori tsohon mataimakin gwamnan jihar Edo, Philip Shaibu daga cikinta.
Jam'iyyar ta ɗauki matakin ne bayan ta zargi Philip Shaibu da cin dunduniyarta ana saura watanni uku a gudanar da zaɓen gwamnan jihar.
Asali: Legit.ng