Home Back

Dakatar Da Ganduje: Alkalin Ya Yi Watsi Da Umurnin Da Ya Bayar

leadership.ng 2024/5/17
Bidiyon Dalar Ganduje: Kotu Za Ta Yanke Hukunci Ranar 22 Ga Satumba 

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 4 karkashin mai shari’a Usman Na’abba, wadda tun farko ta bayar da umarnin wucin gadi na tabbatar da dakatar da Dr. Abdullahi Ganduje a matsayin dan jam’iyyar APC, ta yi watsi da umarnin.

A wata doka da ta gabatar a baya, alkalin ya yanke cewa, tsohon gwamnan jihar Kano, wanda yanzu shi ne shugaban jam’iyyar APC mai mulki ta kasa, an hana shi gabatar da kansa a matsayin shugaban Jam’iyyar, bayan da wasu shugabannin jam’iyyar a matakin  unguwar Ganduje da ke karamar hukumar Dawakin Tofa a jihar Kano karkashin jagorancin mai ba da shawara kan harkokin shari’a, Haladu Gwanjo, suka tsige Shugaban jam’iyyar na kasa a matsayin dan jam’iyyar sannan alkalin ya tabbatar da matakin da suka dauka na dakatar da Ganduje daga APC tun da farko.

Sai dai kuma a wani hukunci na daban da ya yanke a ranar Litinin, alkalin babbar kotun jihar, mai shari’a Usman Na’abba ya soke umurnin da ya bayar tunda farko sannan kuma ya dage sauraron karar zuwa 30 ga Afrilu, 2024 don ci gaba da sauraren karar.

People are also reading