Tinubu Zai Halarci Zikirin Juma’a A Fadar Aminu Ado Ta Nassarawa
Gidauniyar Sheikh Dahiru Usman Bauchi zata gudanar da taronta na Zikirin Juma’a na shekara a fadar Sarki Alhaji Aminu Ado Bayero da ke Nasarawa. An shirya gudanar da taron ne a gobe Juma’a, 5 ga Yuli, 2024, da karfe 4:00 na yamma.
Taron dai zai kasance ƙarƙashin jagorancin Babban Jagoran Tijjaniyya a Najeriya Sheikh Dahiru Usman Bauchi wanda zai kasance babban baƙo na musamman. Manyan baƙin da zasu halarci taron sun haɗa da; Alhaji Aminu Ado Bayero, da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu.
Taron Zikirin zai mayar da hankali ne kan karatuttuka da addu’o’i da nufin magance matsalolin tsaron da Nijeriya ke fuskanta.