Rahoto: Yajin Aikin ’Yan Ƙwadago Ya Jawo Najeriya Ta Yi Asarar Naira Biliyan 149
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida
Ana hasashen Najeriya ta yi asarar akalla Naira biliyan 148.8 na harajin mai a ranar Litinin sakamakon yajin aikin 'yan kwadago.
A cewar wani rahoton hukumar haƙo man fetur (NUPRC), Najeriya na samar da gangar danyen mai 1,281,478 a kowace rana.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
A ranar Litinin din, an sayar da gangar mai na Brent a kan dala 78.27 yayin da bankin CBN ya ba da canjin dala 1 a kan N1,483.5, in ji rahoton The Punch.
Idan aka lissafa N1,483.5 sau adadin gangar mai da kasar ke fitar wa kullum wanda ma'aikatan hakar man ba su yi aiki ba a Litinin, za a ga yawan biliyoyin Naira da aka yi asara.
Ma'aikatan mai karkashin kungiyar PENGASSAN da takwarorinsu na NUPENG da NGW sun rufe dukkanin injunan haƙo mai da ke a fadin kasar a yayin yajin aikin.
A ranar Lahadi, NLC ta umarci dukkanin mambobinta na kungiyar PENGASSAN da NUPENG da su rufe kafatanin wuraren hako mai a ranar Litinin in ji rahoton Channels.
Majiyoyi a fannin mai na kasar sun tabbatar da cewa ma'aikatan sun rufe wuraren hako mai a ranar Litinin, lamarin da ya jawo aikin mai ya tsaya.
A wani labarin, mun ruwaito cewa kungiyoyin kwadagon Najeriya da suka hada da NLC da TUC sun dakatar da yajin aikin da suka tsiga a ranar Talata.
'Yan kwadagon sun shiga yajin aiki ne a ranar Litinin saboda nuna adawa da gazawar gwamnatin tarayya na amincewa da sabon mafi karancin albashi da kuma janye karin kudin wutar lantarki.
Asali: Legit.ng