Home Back

Ana Murnar Dala Ta Karye a Kasuwa, Babban Banki CBN Ya Ɗauki Sababbin Matakai

legit.ng 2024/9/28
  • Yayin da datajar Naira ke ƙaruwa a kasuwa, babban bankin ƙasa CBN ya yi wasu sabababbin sauye-sauye domin inganta ayyukan ƴan canji
  • CBN ya umarci halastattun ƴan canaji su sabunta lasisin aiki kuma ya cire masu dokar ajiye wasu adadin kudi kafin a ba su lasisi
  • Daraktan sashin tsare-tsaren kuɗi na babban bankin, Haruna Mustafa ne ya bayyana haka a wata sanarwa ranar Laraba

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Babban bankin Najeriya (CBN) ya umarci halastattun ƴan canji da ke kasuwancin hada-hadar kudi su sabunta lasisin aikinsu.

Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da dataktan tsare-tsaren kudi na CBN, Haruna Mustafa, ya fitar ranar Laraba, 22 ga wstan Mayu, 2024.

Gwamnan CBN, Yemi Cardoso.
CBN ya umarci ƴan canji su sabunta lasisi aikinsu a Najeriya Hoto: Cenbank Asali: Facebook

Bankin ya kuma bukaci duk wani ɗan canji ya tabbata ya cika sharuɗɗan nau'in lasisinsa daga nan zuwa watanni shida, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Dukkan ƴan canji da masu tallata ƴan kasuwar hada-hadar kuɗi su cike buƙatar neman sabon lasisi na kowane mataki ko nau'in da ya kwanta masu a rai," in ji CBN.

CBN ya yi sabbin sauye-sauye

Har ila yau, babban bankin ƙasar nan ya yi sababbin sauye-sauye a kundin dokoki da ƙa'idojin ayyukan ƴan canjin da aka amince da su.

Ɗaya daga cikin canje-canjen da bankin ya yi shi ne cire tilascin ajiye N200m ga masu lasisi mai dataja ta farko watau Tier-1.

Haka zalika babban bankin ya jingine ajiye N50m ga masu lasisi mai ƙima ta biyu, cewar rahoton Vanguard.

CBN ya kuma janye kudin sabunta lasisi na shekara-shekara na N5m ga ƴan canji da ke matakin fatko da kuma N1m ga ƴan mataki na biyu.

Sanarwan ta ce:

"Babban Bankin Najeriya (CBN) ya fitar da daftarin ka'idojin gudanar da ayyukan ƴan canji a Najeriya a watan Fabrairun 2024, domin jin ra'ayoyin masu ruwa da tsaki.

"Bayan kamma jin shawarwarin masu ruwa a tsaki, a yanzu CBN ya fitar da daftarin ƙa'idojin da aka amince da su domin sa ido kan ayyuka. ƴan canji a Najeriya."

A wani rahoton kuma

Asali: Legit.ng

People are also reading