Home Back

Iran na zaben shugaban kasa

dw.com 2024/7/7
Dan takarar Mohammad Bagher Ghalibaf a lokacin da yake kada kuri'a
Dan takarar Mohammad Bagher Ghalibaf a lokacin da yake kada kuri'a

Ana sa ran 'yan kasar miliyan 61 ne za su kada kuri'ar zaben sabon jagora bayan mutuwar Ebrahim Raisi a watan Mayun 2024, duk da cewa jagoran addinin kasar, Ayatollah Ali Khamenei shi ne mai cikakken fada a ji a Iran kana babban kwamandan rundunar sojin kasar.

'Yan takara hudu ne za su fafata a zaben, sai dai wadanda ake ganin za su iya lashe zaben su ne Saeed Jalili, tsohon mai shiga tsakani a tattaunawar kasa da kasa a kan nukiliya da kuma Mohammad Bagher Ghalibaf, tsohon ministan kiwon lafiyan kasar.

Idan har babu dan takarar da ya samu rinjaye, za a sake komawa zagaye na biyu na zaben a ranar biyar ga watan Yuli.

People are also reading