Home Back

Da Ɗumi-ɗumi: Kotun Ƙoli Ta Ba Ƙananan Hukumomi ‘Yancin Cin Gashin Kansu

leadership.ng 2024/8/21
Da Ɗumi-ɗumi: Kotun Ƙoli Ta Ba Ƙananan Hukumomi ‘Yancin Cin Gashin Kansu

Kotun koli ta bai wa kananan hukumomin kasar nan ‘yancin cin gashin kansu inda kotun ta yanke hanyar biyan kudaden kasonsu daga gwamnatocin jihohinsu.

Kotun kolin ta bayyana haka ne a wata kara da gwamnatin tarayya ta shigar a kan gwamnatocin jihohi 36 a ranar Alhamis, inda ta umurci gwamnatin tarayya da ta biya kudin kason kananan hukumomi 774 kai tsaye zuwa asusun ajiyarsu.

Wani kwamitin alkalai bakwai, a cikin hukuncin da ya yanke, ya kuma bayyana cewa gwamnatocin jihohi na ci gaba da yin amfani da karfinsu wajen rikewa da kuma amfani da kudaden da aka ware wa kananan hukumomin.

Cikakken bayani daga baya…

People are also reading