Home Back

Yawaitar kai wa dalibai hari ya tayar da hankalin mahukuntan Faransa

rfi.fr 2024/5/13

Wani dalibi mai kimanin shekaru 15  ya rasa ransa a Faransa sakamakon raunukan da ya samu, bayan dukan kawo wukan da wasu suka lakada masa.

Wallafawa ranar: 06/04/2024 - 16:48

Minti 1

kofar makarantar Les Sablons inda aka lakadawa wani dalibi dukan kawo wuka da ya kai ga mutuwarsa a Faransa.
kofar makarantar Les Sablons inda aka lakadawa wani dalibi dukan kawo wuka da ya kai ga mutuwarsa a Faransa. © Miguel Medina, AFP

Bayanai sun ce a ranar Alhamis din da ta gabata ne gungun wasu matasa suka yi masa rubdugun a kusa da makarantarsa da ke kudancin birnin Paris, lamarin da ya janyo masa bugun zuciya, wanda kuma bayan garzayawa da shi asibiti ya mutu a ranar Juma’a.

Karo na biyu kenan cikin mako guda da aka aikata irin wannan cin zali a Faransa, inda a ranar Talata, wata daliba mai shekaru 13 ta shiga dogon suma bayan dukan da wasu suka lakada mata a harabar makarantar da take zuwa a birnin Montpellier.

Wadannan lamurra na zuwa ne a yayin da hankalin mahukuntan Faransa ya tashi biyo bayan yawaitar sakwannin barazanar kai wa matsa hari da ake aikewa da su a makarantu da dama.

Domin shawo matsalar ce ma, shugaban Emmanuel Macron ya ce dole a dauki matakan bai wa makarantun kasar kariya daga wannan barazana.

A nata bangaren, rundunar ‘yan sandan Faransa ta sanar da kama wani matashi mai shekaru 17, bisa tuhumarsa da hannu a mutuwar dalibin baya bayan nan da aka kashe.

People are also reading