Home Back

LALUBEN LAƘANIN MATSALAR TSARO A AMURKA: Gwamnonin Arewa 10 za su rankaya taron sanin-makamar-tsaro a Amurka

premiumtimesng.com 2024/5/18
LALUBEN LAƘANIN MATSALAR TSARO A AMURKA: Gwamnonin Arewa 10 za su rankaya taron sanin-makamar-tsaro a Amurka

Cibiyar Inganta Ɗorewar Zaman Lafiya ta Afrika da ke Amurka, ta gayyaci Gwamna Dikko Raɗɗa na Jihar Katsina da wasu gwamnonin Arewa 9, domin halartar taron zaman lafiya da inganta tsaro a Arewacin Najeriya.

Gwamnonin 10 dai dukkan su su fito ne daga jihohin Arewa maso Yamma da kuma Arewa ta Tsakiya, wato yankin da kuma ake kira Middle Belt.

CIkin wata sanarwar da Kakakin Yaɗa Labaran Gwamna na Raɗɗa na Katsina, Ibrahim Kaula ya fitar a ranar Talata, ya ce sauran gwamnonin sun haɗa da Uba Sani na Kaduna, Abba Yusuf na Kano, Nasir Idris na Kebbi, Umar Namadi na Jigawa da kuma Ahmad Aliyu na Sokoto.

Sauran kuma sun haɗa da Dauda Lawal na Zamfara, Hyacinth Alia na Benuwai, Mohammed Bago na Neja, sai kuma Caleb Mitdwang na Filato.

Sanarwar ta ce za su halarci taron na kwanaki uku, wanda za a gudanar a ranakun 23 zuwa 25 ga Afrilu, a Washington, babban birnin Amurka.

Ya ce za ta tattauna matsanancin halin rashin zaman lafiya da tashe-tashen hankunan da ake fama da su a Arewa maso Yamma da kuma Arewa ta Tsakiya, wato matsalar ‘yan bindiga masu garkuwa da mutane.

People are also reading