Home Back

Zakkar fidda kai da Sallar Idi, Tare da Imam Murtadha Gusau

premiumtimesng.com 2024/5/2
Imam Murtada Gusau
Imam Murtada Gusau

Zakkar Fidda Kai

1. Hikimar da tasa ake yin ta: Daga cikin hikimar da tasa ake yin Zakkar fidda kai ita ce: Ta na tsarkake zukatan masu azumi ne daga abinda suka aikata marar kyau, kamar yadda ta ke wadatarwa ce ga talakawa da miskinai daga barin roko da bara a ranar idi.

2. Gwargodon abin da ake cirewa da irin abincin da ake fitarwa: Gwargodon ta shine sa’i daya. Sa’i daya kuma shine mudun Nabiyi hudu, kuma ana kadara sa’i da ‘kilo wat’ uku. Ana kuma fitar wa ne daga mafi rinjayen abincin da mutanen garin suka fi ci a wannan lokacin, kamar su alkama, dabino, shinkafa, zabib da sauran su.

3. Lokacin da aka wajabta fitar da ita: Zakkar fidda kai ta na wajaba ne da zarar daren idi ya shiga (wato da zarar an ga watan karamar Sallah (Shawwal)). Lokacin bayarwa kuma yana halasta ne tun kafin ranar Sallah da kwana daya ko biyu, domin aikin Abdullahi Dan Umar Allah ya kara masu yarda da ya nuna hakan. Kuma lokacin bayarwar da yafi shine daga fitowar alfijir na ranar idi har zuwa dab da Sallar idi, domin umurnin Manzon Allah (SAW) da yayi na a bayar da ita ga mutane kafin fita zuwa Sallah.

4. Wadanda Zakkar fidda kai ta wajaba a kansu: Ita Zakkar fidda kai tana wajaba ne ga dukkan mutumin da yake Musulmi, Da, ko Bawa, mace ko namiji, babba ko karami, wanda Allah ya azurta da abincin da ya rage bayan na wuni da dare, kuma yana halasta a fitar wa da Dan da yake cikin mahaifa, wato cikin mahaifiyar sa.

5. Wadanda ake ba Zakkah: Zakkar kono (wato Zakkar fidda kai), ana bayar da ita ne ga duk wanda ya cancanci a ba shi sauran Zakkah ta dukiya, daga cikin mutane takwas din nan, amma talakawa da miskinai sun fi cancanta daga sauran da aka ambata, domin fadin Ma’aikin Allah (SAW):

“Ku wadatar da su daga barin roko na wannan ranar (Ranar Idi).”

• Sallar Idi

1. Hikimar da ke cikin Shar’anta Sallar Idi: Sallar idi na daga cikin alamomin addinin Musulunci bayyanannu wadanda Allah ya kebance alummar Annabi Muhammad (SAW) da su, wurin tabbatar da godiya ga Allah majibinci akan kammala ibadar azumin watan Ramadan (A karamar Sallah kenan), da kuma ziyartar dakin Allah mai alfarma da nufin ibadar aikin Hajji (A babbar Sallah kenan). Kamar yadda ya kasance a cikin idi, akwai kira zuwa ga tausayi da jin kai tsakanin al’ummar Musulmi da haduwar su a wuri daya, da kuma daidaita zukata.

2. Hukuncin Sallar Idi: Sallar idi farillah ce ta kifaya wadda idan wasu suka yi sun dauke wa wasu. Manzon Allah (SAW) da Halifofin bayan sa sun kasance suna aikata ta. Kuma ita Sunnah ce mai karfi akan kowane Musulmi, namiji ko mace, kuma an shar’anta ta ga mazauna ban da matafiya. Sannan kuma ita ba farillah bace da idan mutum bai yi ba yayi zunubi ko ya sabawa Allah. Sannan idan aka dakatar da Sallar idi a cikin cunkoson jama’ah, aka sanar da cewa kowa yayi Sallar idin sa a gida, tare da iyalan sa, sanadiyyar wata cuta ko wata lalura ko wata annoba, to ba’a yi laifi ba kuma ba’a sabawa Allah ba, ba’a yi zunubi ba, kuma wallahi ba’a yi kuskure ba. Duk kuma wanda yace an sabawa Allah idan ba’a yi Sallar idi ba saboda wata lalura, to yazo muna da hujja ko dalili!

3. Sharuddan Sallar Idi: Shuruddan Sallar idi kamar juma’ah ce, sai dai ban da huduba, hudubobi biyu, domin su Sunnah ne a Sallar idi, kuma ana yin su ne bayan Sallah, ita kuma juma’ah kafin Sallah.

4. Lokacin Sallar idi: Lokacin ta shine, daga dagowar rana da safe gwargwadon tsawon mashi, har zuwa zawali (wato gushewar rana daga tsakiya). Idan ba’a san da idi ba har bayan zawali sai a Sallace ta gobe a matsayin ramako na lokacin ta.

5. Yadda ake yin Sallar Idi: Sallar idi raka’ah biyu ce, domin fadin Sayyidinah Umar (RA):

“Sallar Fitri (wato karamar Sallah) da Sallar Adha (wato babbar Sallah) raka’o’i biyu ne cikakku ba tare da ragi ko kari ba, akan harshen Annabin ku (SAW), duk wanda ya kirkiro wani abu to ya tabe.” [Imam Ahmad]

Ana yin Sallar idi ne kafin ayi hudubah. Za’a yi kabbara a raka’ar farko bayan kabbarar harama, kuma kafin ta’awuzi kabbarori shida. A raka’ah ta biyu kuma za’a yi kabbarah kafin karatu sau biyar. Kuma duk wanda zai yi Sallar idi a gida da shi da iyalin sa saboda lalurar annobar korona, to babu laifi, hakan yayi daidai. Kuma yadda ake yin Sallar idi a filin idi, nafilah, raka’ah biyu, haka zai yi ta a gidan sa babu wani babanci, huduba ce kawai ba zai yi ba. Kuma Sallar idin sa tayi, sannan wallahi duk duniya, babu wani malami da ya isa yace wadanda suka yi Sallar idi a filin idi, cikin jama’ah, sun fi shi lada ko wani matsayi. Wannan sam ba gaskiya bane. Allah yasa mu dace, kuma ya yaye muna wannan annobar ta korona, amin.

6. Wurin da ake yin Sallar idi: Asali ana yin Sallar idi a fili ne, idan babu wata matsala ko wata lalura daga cikin lalurori. Amma kuma a sani, ya halasta ayi ta a cikin Masallaci ko a gida idan bukatar hakan ta kama. Misali, a irin halin da muka samu kan mu a ciki yau, sanadiyyar lalurar annobar korona da ta ke addabar duniya baki daya. Duk wadannan mutane da suke ta kururuwa da ihun banza, suna cewa wai lallai, dole-dole sai an yi Sallar idi a cikin cunkoson jama’ah, yadda aka saba yi, wannan suna yi ne kawai saboda jahilci ko son zuciyar su. Kasashen Musulmi irin Saudiyyah, Masar, Indonesiya, Hadaddiyar Daular Larabawa, Morocco da sauran su, ba mu fi su addini ba, amma wallahi tuni Malaman kasashen suka yi taro, suka ba da fatawar cewa, kowa yayi Sallar idin sa a gidan sa. Kuma shugabannin wadannan kasashe tuni sun zartar da hukunci akan wannan fatawa ta wadannan Malamai. Amma mu anan Najeriya abun ba haka bane, mu komai sai mun siyasantar da shi, ko mu nuna cewa mu jahilai ne, ko kuma mu bi son zuciyar mu. Ina rokon Allah ya kare mu daga sharrin jahilci da bin son zuciya, amin.

7. Sunnonin Sallar Idi: An sunnanta yin kabarbari ba tare da kayyade cewa sai bayan idar da Salloli ba, da kuma bayyanar da kabarbarin tun a daren Sallah din, saboda fadin Allah mai girma da daukaka:

“Kuma domin ku cika lissafi, kuma ku girmama Allah (wato ku yi masa kabarbari) akan abinda ya shiryar da ku.” [Suratu Bakarah, 185]

Kuma Imamu Ahmad yace:

“Abdullahi Dan Umar Allah ya kara masu yarda, ya kasance yana kabarbari a duk idin guda biyu.”

Kuma game da goman farko na Zul-Hijjah, sai Allah madaukakin Sarki yace:

“Kuma su ambaci Allah a wadansu kwanuka sanannu.” [Suratu Hajji, 28]

Amma kabarbari da aka kayyade sune wadanda suka kebanci bayan Salloli, wannan ko ya kebanci idin babbar Sallah ne kadai, ban da karamar Sallah. Sai a fara ga wanda baya wurin aikin Hajji, daga Sallar asuba ta ranar arafah, har zuwa karshen kwanakin babbar Sallah.

Sannan an so mamu ya isa Masallacin idi da wuri kafin zuwan liman, amma idan har shugabanni sun yarda ayi Sallar a filin idi kamar yadda aka saba, amma shi liman sai ya jinkirta, ba zai isa wurin Sallar ba har sai lokacin ta yayi. Kuma an so mai tafiya Sallar idi yayi tsafta domin halartar ta, ya kuma sanya sabbin tufafi ko mafiya kyawun tufafinsa, kuma ya sanya turare, kuma mata kada su bayyanar da adonsu, kuma kar su sanya turare.

8. Sunnonin idi: An so a gabatar da Sallar idin babbar Sallah da wuri, kuma a jinkirta ta a karamar Sallah. Kuma an Sunnanta cin abinci kafin a fita a karamar Sallah, kodai aci dabino, da kuma kame baki daga barin cin abinci a lokacin babbar Sallah, domin a fara ci daga abin da aka yanka na layyah.

Wallahu ‘Alamu. Allah yasa mu dace, amin.

Ina rokon Allah ya kyauta, kuma ya kawo muna mafita ta alkhairi a dukkanin al’amurran mu, amin.

Dan uwan ku, Imam Murtadha Muhammad Gusau, ya rubuto daga Okene, Jihar Kogi, Najeriya. Za’a iya samun sa a lambar waya kamar haka: 08038289761.

People are also reading