Home Back

Jam'iyyaun masu matsakaicin ra'ayi ke da rinjaye a EU

dw.com 2024/7/7
Shugabar hukumar gudanarwar kungiyar ta EU, Ursula von der Leyen
Shugabar hukumar gudanarwar kungiyar ta EU, Ursula von der Leyen

Duk da gagarumin nasarar da jam'iyyar masu tsattsaurar ra'ayi suka samu a kasashen Faransa da Jamus da kuma Austria a zaben majalisar dokokin kungiyar Tarayyar Turai, har yanzu jam'iyyu masu matsakaicin ra'ayi ne ke kan gaba a majalisar dokokin ta EU. Sakamakon zabukan dai na ci gaba da nuni da cewa, jam'iyyar al'umma ta European People's Party (EPP), za ta tsaya a matsayinta na mafi rinjaye a majalisar.

Bisa dukannin alamu, shugabar hukumar gudanarwar kungiyar ta EU, Ursula von der Leyen na kan hanyar ci gaba da jagorancin kungiyar har zuwa shekarar 2029.

A makwanni masu zuwa ne, von der Leyen za ta nemi samun goyon bayan mafi yawan 'yan majalisar, domin amince mata a matsayin shugaba a karo na biyu.

People are also reading