Hukuncin Masarautar Kano ya Lasawa Bangarorin Da Ke Rikici Zuma a Baki
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Jihar Kano- Hukuncin da babbar kotun tarayya ta yanke kan batun rikicin masarautar Kano ya bar baya da kura, inda bangarorin biyu da ke cikin dambarwar ke ganin su ne da nasara.
A shari’ar da ya yanke ranar Alhamis, Mai shari’a Abdullahi Muhammad Ladan ya jingine dokar da aka yi amfani da ita wurin maido da Malam Muhammadu Sanusi II karagarsa.
Daily Trust ta wallafa cewa Mai shari’a Muhammad Ladan ya ce hukuncin bai soke dokar da rushe masarautun Kano da majalisar dokokin jihar ta samar ba.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Gwamnatin jihar Kano ta hakikance kan cewa hukuncin da kotu ta yanke a yammacin Alhamis ya tabbatar da tsige sarkin Kano 15, Aminu Ado Bayero yayin da ta umarci a fitar da shi daga fadar sarki ta Nassarawa.
A sanarwar da darakta janar na gwamna kan yada labarai, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya wallafa a shafinsa na facebook, babu inda hukuncin ya soke dokar da ta tumbuke rawanin Sarki Bayero.
A rahoton da Leadership News ta wallafa, tsagin Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero ya shiga murnar samun nasara a kotun tarayya, haka ma gwamnatin Kano.
Tun da fari, Sarkin Dawaki babba, Aminu Babba Dan’agundi ta bakin lauyansa, Idris Aliyu Nassarawa ya nemi kotu ta rushe dokar da ta tsige masarautun Kano.
A baya mun kawo labarin cewa babbar kotun tarayya da ke zamanta a kano karkashin mai shari’a Abdullahi Muhammad Liman ta yanke hukunci kan dambarwar masarauta.
Mai shari’a na ganin gwamnati ta yi biris da umarninsa na farko, wanda ya sa ya jinge dokar da ta maido da Sanusi II karagarsa, amma ta ce hakan bai soke dokar da ta rushe masarautu ba.
Asali: Legit.ng