Home Back

Tinubu Ya Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Babban Ɗan Jarida Kabir Yusuf

leadership.ng 2 days ago
Tinubu Ya Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Babban Ɗan Jarida Kabir Yusuf

Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyyarsa ga iyalan Malam Kabir Yusuf, wani gogaggen ɗan Jarida da ya rasu a jiya Talata. Malam Yusuf ya yi suna a matsayin wakilin babban birnin tarayya na Jaridar Triumph da Rediyon Faransa. Ya kuma shafe shekaru da dama yana aiki a gidan gwamnati.

A cikin sakonsa, shugaba Tinubu ya yi addu’ar Allah ya jikan Malam Yusuf, ya kuma yi wa iyalansa ta’aziyya a wannan lokaci na jimanin rashinsa.

Ajuri Ngelale, mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman ne ya fitar da sanarwar a yau 3 ga Yuli, 2024.

People are also reading