Home Back

Gwamnatin Tarayya za ta fara gagarimin aikin haƙo ɗanyen man fetur a Jihar Ogun – Lokpobiri

premiumtimesng.com 2024/6/18
Crude oil
Crude oil

Gwamnatin Tarayya za ta fara gagarimin aikin haƙar ɗanyen man fetur a Jihar Ogun, kamar yadda Ƙaramin Ministan Fetur, Lokpobiri ya tabbatar.

Ya ce hakan ya zo ne daidai lokacin da gwamnatin tarayya ke buƙatar ƙarin kuɗaɗen shiga a ɓangaren ɗanyen mai da gas.

Lokpobiri ya ce za a fara aikin haƙar a wasu wurare a faɗin Jihar Ogun, saboda Jihar ko tantama babu akwai ɗanyen mai a cikin ta.

Ƙaramin Ministan Fetur, Heineken Lokpobiri, ya bayyana haka a ranar Juma’a, yayin da ya kai ziyara Ofishin Gwamnan Jihar Ogun, a Abeokuta, babban birnin Jihar.

Lokpobiri ya kai ziyarar tare da manyan masu hannu a harkokin man fetur da gas daban-daban, cikin su har da Shugaban NNPCL, Mele Kyari.

Ya ce Jihar Ogun na ɗaya daga ɓangaren Dahomey Basin, wurin da ake da kyakkyawan zaton akwai ɗanyen mai kwance maƙil a ƙasa.

Ya ce sun kai ziyara Jihar Ogun ne domin su nuna irin gaggawar fara aikin wanda Gwamnatin Tarayya ke so a yi, domin ƙara samun hanyoyin kuɗaɗen shiga ta hanyar ɗanyen mai.

Ya ce ɗanyen mai ne hanya mafi saurin kawo wa Najeriya kuɗaɗen shiga masu tarin yawa.

A zamanin mulkin Buhari an ƙaddamar da aikin haƙar ɗanyen mai a yankin Kolmani da ke tsakanin jihohin Bauchi da Gombe.

Sai dai kuma tun bayan ƙaddamar da aikin, har yau shiru ka ke ji babu labari kuma babu ƙarin bayani.

People are also reading