Home Back

'Yan Kwadago Sun Ayyana Shiga Yajin Aikin Sai Baba Ta Gani Kan Abubuwa 2 a Najeriya

legit.ng 2024/7/2
  • Ƴan kwadago a Najeriya sun sanar da shiga yajin aiki daga ranar Litinin, 3 ga watan Yuni, 2023 saboda gazawar gwamnatin tarayya
  • NLC da TUC sun ɗauki wannan matakin kan rashin karkare batun mafi ƙarancin albashi da kuma ƙarin kuɗin wutar lantarki ga ƴan Band A
  • Gwamnati ta gabatar da tayin N60,000 a matsayin ƙarancin albashi amma NLC ta tsaya kai da fata kan N494,000

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Kungiyoyin kwadagon Najeriya sun ayyana shiga yajin aikin sai baba-ta-gani a fadin kasar nan daga ranar Litinin 3 ga watan Yuni, 2024.

Ƴan kwadagon sun ɗauki matakin tsunduma yajin aiki ne kan gazawar gwamnatin tarayya na ƙarƙare batun mafi karancin albashi da ƙara kuɗin wutar lantarki.

NLC da TUC sun shiga yajin aiki.
Ma'aikatan Najeriya sun ayyana shiga yajin aikin sai baba-ta-gani daga ranar Litinin Hoto: Nigeria Labour Congress Asali: Twitter

Jaridar Vanguard ta tattaro cewa tun da farko manyan kungiyoyin kwadagon ƙasar nan NLC da TUC sun nun alamun fara yajin aiki daga farkon makon gobe.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ƙungiyoyin sun nuna cewa matuƙar kwamitin mafi ƙarancin albashin da gwamnati ta kafa ya gaza amincewa da buƙatun ƴan kwadago, to tabbas za su shiga yaji.

A taron manema labarai, shugaban NLC da takwaransa na TUC, sun roki ‘yan Nijeriya da su jure duk halin da za a shiga.

Sun kuma bai wa mutane haƙuri da cewa, “Muna baku haƙuri kan duk abin da bai maku daɗi ba amma za mu yi haka ne domin kawo ƙarshen lamarin."

Ƙarin bayani na nan tafe...

Asali: Legit.ng

People are also reading