Home Back

Dakarun Sojoji Sun Hallaka Rikakken Shugaban 'Yan Bindiga da Mayakansa 35 a Arewa

legit.ng 2024/7/3

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Jihar Kaduna - Dakarun sojoji na rundunar Operation Whirl Punch, sun hallaka riƙaƙƙen shugaban ƴan bindiga, Buhari Alhaji Halidu, wanda aka fi sani da Buharin Yadi a jihar Kaduna.

Sojojin sun hallaka gawurtaccen ɗan bindigan ne yayin wani artabu a ƙaramar hukumar Giwa ta jihar.

Sojoji sun hallaka shugaban 'yan bindiga a Kaduna
Dakarun sojoji sun hallaka shugaban 'yan bindiga, Buharin Yadi a Kaduna Hoto: @HQNigerianArmy Asali: Facebook

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar, Samuel Aruwan, ya fitar, cewara rahoton tashar Channels tv.

Kwamishinan ya bayyana cewa Buharin Yadi tare da mayaƙansa mutum 35 sun gamu da ajalinsu ne bayan sun fafata da dakarun sojojin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Dakarun sojojin ƙarƙashin jagorancin kwamandan rundunar, Manjo Janar Mayirenso Saraso, sun je aiki ne a dajin Idasu da ke iyaka da ƙaramar hukumar Giwa a Kaduna da ƙaramar hukumar Sabuwa a jihar Katsina.

Asali: Legit.ng

People are also reading