Saudiyya Ta Fadi Adadin Mahajjatan Bana, Ta Fadi Damuwa 1 da Za a Fuskanta
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Saudi Arabia - Kasar Saudiyya ta yi karin haske kan adadin mahajjatan da suka iso kasar daga dukkan fadin duniya.
Saudiyya ta fadi haka ne yayin da ake kokarin fara aikin Hajjin shekarar 2024 a gobe Juma'a, 14 ga watan Yuni.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa jami'in sadarwa na ma'aikatar lafiyar kasar ya shawarci mahajjata kan zafi da ake a kasar.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Jami'in ma'aikatar samar da fasfo a kasar Saudiyya ya bayyana cewa a bana an samu adadin mutane 1,547,925 da suka iso kasar domin aikin Hajji.
Jami'in ya ce wannan shi ne adadin mutanen da suka zo kasar ta tashar jiragen sama, motoci da kuma tashar jiragen ruwa, rahoton Daily Sun.
Jami'in yada labaran ma'aikatar lafiyar kasar Saudiyya, Dr. Muhammad Al-Abdullaali ya ce babbar matsalar da za a fuskanta a bana itace zafi.
Muhammad Al-Abdullaali ya ce an samu karin zafi a kasar yayin da aikin Hajjin bana ke kokarin kankama.
Muhammad Al-Abdullaali ya bayyana cewa kasar tanadi lemar hannu, ruwan sha da inuwa da za a rika hutawa.
Saboda haka ya shawarci mahajjatan da su rika bin dokokin da hukumar lafiya ta gindaya domin kammala aikin Hajji cikin sauki.
A wani rahoton, kun ji cewa jami'an tsaron kasar Saudiyya sun yi atisaye domin nuna shirin ba da kariya ga dukkan mahajjatan shekarar 2024.
Hukumomin a kasar sun tabbatar da ɗaukan sababbin matakan kara tsaro a wurare da dama ciki har da asibitoci da wuraren karbar magani da dama.
Asali: Legit.ng