Mutane Kimanin 40 Sun Mutu, Sama da 100 Suna Asibiti Bayan Sun Yi Tatul da Giya
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Kasar India - An samu barkewar annoba a jihar Tamil Nadu bayan mutane da dama sun sha giyar gargajiya.
Rahotanni sun yi nuni da cewa lamarin ya fara ne bayan mutane sun sha giyar a jiya Laraba, 19 ga watan Yuni.
Rahoton Daily Mail ya nuna cewa gwamnatin kasar ta tabbatar da faruwar lamarin da kuma bayyana matakin da ta dauka.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Jami'in gwamnatin Indiya ya tabbatar da cewa an samu barkewar annoba a yankin Kallakurichi da ke jihar Tamil Nadu.
Ya ce tun jiya Laraba ake samun mutane na amai da gudawa da ciwon ciki bayan shan giyar gargajiyar, rahoton BBC.
Gwamnatin kasar ta tabbatar da cewa kimanin mutane 36 ne suka rigamu gidan gaskiya biyo bayan shan giyar.
Ta kuma bayyana cewa a halin yanzu akwai mutane sama da 100 da suke kwace a asibiti tun da suka sha giyar.
Gwamnatin kasar ta tabbatar da kama mutane sama da 10 ciki har da basarake da shugaban yan sandan yankin.
Kano: Rundunar ƴan sanda ta yi martani kan zargin Kwankwaso na sanya dokar ta ɓaci
Hukumomin kasar sun tabbatar da kama shugabannin yankin inda suka ce an kamasu ne bisa laifin gaza hana faruwar lamarin.
Haka zalika rundunar yan sanda ta kama mutane hudu da ake zargi suna da hannu wajen samar da gurbatacciyar giyar.
A wani rahoton, kun ji cewa gwamnatin jihar Nasarawa ta cigaba da ɗaukan matakai kan masu hako ma'adanai domin tabbatar da ingancin tsaro.
Biyo bayan haka, gwamantin ta dauki matakin gaggawa kan kamfanin Trimadix Geomin Consult Limited da ke aiki a jihar Nasarawa.
Asali: Legit.ng