Home Back

Fafaroma ya yi tir da kisan faren hula a Gabashin Kwango

dw.com 2024/6/29
Fafaroma ya yi tir da rikicin Gabashin Kwango
Fafaroma ya yi tir da rikicin Gabashin Kwango

Babban Limanin na cocin Kotolika ya ce suna samun labarai masu bakanta rai a gamme da yadda ake kisan kare dangi wa fararen fula galibi mabiya addinin Krista a wannan yankin na Kwango, inda rikici ke daukar sabon salo a baya-bayan nan.

Kazalika Fafaroma Francis ya yi kira da babbar ga gwamnatin Kwango da kuma masu fada a ji a duniya da su yi duk mai yuwa don kawo kawo karshen wannan tashin hankali tare kuma da kare fararen hula da ba su ji ba su gani ba.

Kawo yanzu dai sama da mutane 150 rikicin na gabashin Kwango ya ritsa da rayukansu cikin har da mutum 42 da aka halaka a daren Laraba wayewar Alhamis din da ta gabata, lamarin da kungiyoyin fararen hula ke dora alhaki ga kungiyoyin 'yan ta'adda na AFD da kuma IS. 

People are also reading