Home Back

Gwamna Dauda Ya Sanar Da Ɗaukar Ma’aikata Da Samar Da Garejin Tireloli A Zamfara

leadership.ng 2024/4/28
Gwamna Dauda Ya Sanar Da Ɗaukar Ma’aikata Da Samar Da Garejin Tireloli A Zamfara

Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara, ya amshi rahotannin ayyuka daban-daban da gwannatinsa ke aiwatarwa a duk faɗin jihar a yayin taron Majalisar zartarwar jihar a ranar Litinin a zauren majalisar da ke gidan gwamnati a Gusau.

Mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya ffitar da sanarwar cewa majalisar zartarwar ta zauna a karo na 16 tun hawan gwamnatin Gwamna Dauda Lawal.

A cewarsa, shugaban majalisar, Gwamna Lawal, ya samu cikakkun rahotanni kan ci gaban da aka samu, da ƙalubalen da aka fuskanta, da kuma lokacin da ake sa ran kammala kowane aiki.

Waɗannan ayyuka da ake gudanarwa sun shafi sassa daban-daban, gami da ababen more rayuwa, kiwon lafiya, ilimi, da tilasta bin doka.

A yayin jawabin da ya yi wa majalisar, Gwamna Lawal ya jaddada muhimmancin ‘aikin ceto Zamfara’ na gwamnatinsa, wanda ya ba da fifiko wajen tabbatar da gaskiya da riƙon amana.

“Muna da babban nauyi a gabanmu yayin da muka fara aikin ceto. Burin mu shi ne cetowa, tare da sake gina Zamfara, kasancewar ba mu da wani wurin da za mu kira gida sai nan.

“Na amince da ɗaukar ma’aikata 250 aiki a Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta Zamfara (ZAROTA) nan take domin inganta ayyukan gine-ginen da gwamnatina ke gudanarwa a cikin birane.

“Na umurci kwamishinan shari’a da babban lauyan gwamnati da su kafa kotun da za ta kula da laifukan da suka shafi ababen hawa.

“Bugu da ƙari, za mu samar da wurare na manyan motoci guda biyu a Gusau domin daƙile cunkoson ababen hawa da tireloli ke haddasawa.”

 
People are also reading