Kudin Wuta: KEDCO Ya Maka Kungiyar da Yake Zargi da Jawo Masa Asarar Biliyoyi a Kotu
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Abuja- Kamfanin rarraba hasken wutar lantarki (KEDCO) ta maka kungiyar masu sarrafa kayan abinci na kasa (MAN) gaban kotun babbar tarayya da ke Abuja.
Kamfanin na zargin kungiyar da shigar masu aiki da har ta kai sun tafka mummunar asarar N5.3bn a baya-bayan nan.
Punch News ta wallafa cewa KEDCO ya dauki matakin ne bayan kungiyar MAN ta ki amincewa da biyan karin kudin wuta da su ka yi.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Kamfanin rarraba hasken wutar lantarki na KEDCO ya bayyana cewa kin biyan sabon kudin wuta da aka yanke ya jawo asarar N5.3bn a duk wata.
Sun dora laifin hakan kan hukuncin kotu da kungiyar masu sarrafa kayyaki ta kasa ya samo ya dakatar da biyan kudin.
Daily Trust ta wallafa cewa ayyukan kamfanin ya jawo mata asara mai dimbin yawa da kai biliyoyin Naira duk wata.
Shugaban sashen yada labaraina KEDCO, Sani Bala Sani ya ce matakin da MAN ta dauka ya tauye mata hanyoyin samun kudi.
A wani rahoton kun ji cewa wata babbar kotu a Kano ta dakatar karbar sabon kudin wuta da hukumomi su ka kara ga 'yan kasar nan.
Kamfanonin da su ka shigar da kara sun hada da Supper Sack Limited, BBY Sack Limited, Mama Sannu Industries Limited, Dala Good Nigeria, Tofa Textile da Manufacturers Association of Nigeria.
Asali: Legit.ng