Home Back

Ana Tsaka da Rigimar Sarauta a Kano, Gwamna Ya Ragewa Sarakuna Ƙarfin Iko

legit.ng 2024/7/5
  • Gwamna Abdullahi Sule ya hana sarakuna bayar da shaidar haƙar ma'adanai da mutanen ba su cika sharuɗɗa ba a jihar Nasarawa
  • Sule ya gargaɗi sarakaunan kan barazanar da hakan kan iya haifarwa a jihar idan har ba a gaghauta ɗaukar mataki kan lamarin ba
  • Ya ce masu haƙar ma'adanai ba kan ƙa'ida suke jawo rashin zaman lafiya domin ɗauke hankalin mahukunta daga albarkatun ƙasa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Nasarawa - Yayin da hankula suka fi karkata kan rigimar sarautar Kano, Gwamna Abdullahi Sule ya ɗauki mataki kan sarakuna a jihar Nasarawa.

Gwamna Sule ya gatgaɗi sarakuna su guji bayar da takardar izinin haƙo ma'adanai ga. mutanen da ba su cika sharuɗɗa ba a kananan hukumomi 13 na jihar.

Gwamna Abdullahi Sule.
Gwamna Sule ya hana sarakuna bada izinin haƙar ma'adai da mutanen da ba su sani ba Hoto: Abdullahi A. Sule Asali: Facebook

Abdullahi Sule ya bayyana babbar barzanar tsaro da jihar ke fuskanta sakamakon bada izinin ga waɗanda basu dace ba, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamnan ya yi wannan gargadin ne a lokacin da ya karbi bakuncin majalisar sarakunan jihar karkashin jagorancin mataimakin shugabanta, Sarkin Keffi, Dokta Shehu Chindo Yamusa III.

Yayin da yake jawabi ga sarakunan a gidan gwamnatinsa da ke Lafiya, Sule ya nuna damuwa kan kwararar haramtattun masu haƙar ma'adanai a jihar.

Ya ce hakan ka iya zama babbar barazana ga tsaro matukar ba a yi gaggawar tsohe duk wata hanyar shigowar masu haƙar ma'adanai ba bisa ƙa'ida ba.

Ya bukaci sarakunan da su yi taka-tsan-tsan da daidaikun mutane da ke amfani da matsin tattalin arziki wajen tayar da zaune tsaye a wuraren hakar ma’adinai.

"Ba abin da ke kawo rashin zaman lafiya kamar haƙar ma'adanai, ita ce hanya mafi sauƙi da mutane ke samun kuɗi.
"Musamman waɗanda babu kishin jiharmu a zuciyarsu burinsu kawai su hana zaman lafiya ta yadda za su ci gaba da haƙo ma'adanai ba tare da an waiga kansu ba."

- Abdullahi Sule.

Bugu da ƙari, gwamnan ya shaidawa sarakunan cewa ana ci gaba da gano albarkatun ƙasa a jihar kuma kamfanoni na nuna sha'awar zuba hannun jari, Channels tv ta ruwaito.

Gwamnatin za ta ɗaukaka ƙara

A wani rahoton kuma Gwamnatin Kano karƙashin jagorancin Abba Kabir Yusuf ta ce za ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin soke naɗin Muhammadu Sanusi II.

Kwamishinan yaɗa labarai na jihar Kano, Alhaji Baba Ɗantiye ne ya tabbatar da haka a wani saƙo da ya turawa manema labarai.

Asali: Legit.ng

People are also reading