Home Back

Gobara Ta Kama a Matatar Man Dangote, Kamfanin Ya Yi Martani Kan Lamarin

legit.ng 2024/10/6
  • Wani bangare na matatar man Alhaji Aliko Dangote ya kama da wuta a jihar Lagos a yau Laraba 26 ga watan Yunin 2024
  • Wutar ta tashi ne bangaren ETF da ke tace gurbataccen ruwa na matatar inda aka tabbatar da kashe wutar da gaggawa
  • Kakakin kamfanin, Anthony Chiejina shi ya tabbatar da haka inda ya ce babu rasa rai ko rauni daga iftila'in

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Lagos - An shiga tashin hankali bayan wani bangare na matatar man Aliko Dangote ya kama da wuta.

Lamarin ya faru ne a yau Laraba 26 ga watan Yunin 2024 a sashen tsaftace ruwa na matatar da ake kira ETF.

Kakakin kamfanin Dangote, Anthony Chiejina shi ya tabbatar da haka a shafin X a yau Labara 26 ga watan Yunin 2024.

Chiejina ya ce wutar ta kama ne a bangaren ETF da ke tace girbataccen ruwa a matatar da ke jihar Lagos.

Ya tabbatar da cewa an shawo kan matsalar inda ya ce ba wata babbar matsala ba ce kuma babu asara.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Mun yi nasarar shawo kan matsalar wutar da yake ba babba ba ce a yau Laraba 26 ga watan Yunin 2024 a sashen ETF."
"Ba wani abin damuwa ba ne tun da matatar na ci gaba da aiki kuma babu rauni ko mutuwa daga bangaren ma'aikatanmu."

- Anthony Chiejina

Karin bayani na tafe...

Asali: Legit.ng

People are also reading