Home Back

ANC na shirin kafa gwamnatin hadaka

dw.com 2024/7/1
Afirka ta Kudu | Shugaban  Kasa | Cyril Ramaphosa | ANC | Zabe
Shugaban Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa

A karon farko jam'iyya mai mulki ta ANC ta rasa rinjaye a zaben da ya gudana, bayan kwashe shekaru 30 tana jan akalar kasar. Shugaba Cyril Ramaphosa da sauran shugabannin jam'iyyun adawa sun halarci zauren da Hukumar Zabe ta sanar da sakamakon a hukumance, sai dai jam'iyyar tsohon shugaban kasar Afirka ta Kudun Jacob Zuma ta yi fatali da sakamakon da ta bayyana da haramtacce. Sai dai a nasa bangaren shugaban jam'iyyar DA wacce ta zo ta biyu a zaben, John Steenhuisen ya ce, a shirye suke su tunkari duk kalubalen da zai taso. Ana dai tsammanin DA din da EFF ne jam'iyyu na farko da ANC za ta nemi kafa gwamnatin hadaka da su, duk kuwa da cewa akwai yiwuwar tuntubar MK ta tsohon shugaban kasar Zuma.

People are also reading