Home Back

Tsohon Kwamishina Ya Fallasa Gwamnati, An Gano Uba Sani Yana ‘Karya’ da Ayyukan El Rufai

legit.ng 2024/8/22
  • Jafaru Sani ya fito ya kare Nasir El-Rufai wanda ‘yan majalisar dokokin jihar Kaduna suka taso shi a gaba
  • Tsohon kwamishinan ya musanya zargin da ake yi a kan batun bashi, ya yi bayanin irin ayyukan da aka yi
  • ‘Dan siyasar ya zargi Uba Sani da fakewa da ayyukan da aka yi tun a gwamnatin El-Rufai, yana nuna nasu ne

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada

Kaduna - Jafaru Sani ya dauki lokaci ya kare gwamnatin Nasir El-Rufai daga zargin cewa ta yi awon gaba da dukiyar al’ummar Kaduna.

Akwai zargin da majalisar dokoki ta ke yi na cewa an karkatar da N423bn a lokacin da Nasir El-Rufai ya yi mulki daga 2015 zuwa 2023.

Uba Sani da El-Rufai
An zargi Uba Sani da neman suna da ayyukan Nasir El-Rufai a Kaduna Hoto: @BashirElRufai/@IU_Wakilii Asali: Twitter

Kwamishinan Nasir El-Rufai ya kare shi

A wani fai fai da wani Imran U Wakili Oluwa Femi ya wallafa a shafin X, Jafaru Sani ya musanya wadannan zargi, har ya yi martani.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Rahoton kwamitin binciken majalisar Kaduna ba komai ba ne face karya da soki-burutsu a wajen Jafaru Sani wanda ya yi kwamishina.

El-Rufai da zargin 'yan majalisar Kaduna

Amma a wata hira da aka yi wani ‘dan majalisar dokokin Kaduna a tashar Channels, ya bayyana akasin ikirarin Malam Ja’afar Sani.

Honarabul Henry Marah ya ce majalisa ba ta amince da wasu daga cikin bashin da gwamnatin Malam Nasir El-Rufai ta karbo ba.

Tsohon kwamishinan ya ce suna nan a kan bayanin da El-Rufai ya yi game da basussukan jihar a lokacin da yake mika mulki.

Uba Sani yana dauraye ayyukan El-Rufai?

Har ila yau, Jafaru Sani ya caccaki gwamnatin Uba Sani da ya zarga da ikirarin ita ta yi wasu ayyuka da a zamanin El-Rufai aka yi su.

An yi misalai da katafaren dakin bincike, makarantun kimiyya da wasu 62 a karkashin tsarin Agile da kayan asibitocin shan magani 250.

Sannan ya yi karin haske cewa cikin ayyukan da Uba Sani yake tunkaho da su akwai wadanda tun kafin El-Rufai aka samo kudinsu.

Malam Jafaru Sani yana maida martani ne ganin gwamnatin Kaduna ta na kukan an ci bashi kuma ba a san ina kudin suka shige ba.

Gwamna Uba ya koka da bashin El-Rufai

Kwanaki aka samu labari Gwamna Uba Sani ya fadi bashin da aka ci a Kaduna da kudin da Nasir El-Rufai ya bari a asusun jihar Kaduna.

Uba Sani ya ce kason jihar na tafiya ne a biyan bashin da aka ci. Sai dai shi ya dafe aka karbo bashin a lokacin yana majalisar dattawa.

Asali: Legit.ng

People are also reading