Home Back

Bola Tinubu Na Jagorantar Taron FEC a Fadar Shugaban Kasa, Bayanai Sun Fito

legit.ng 6 days ago

FCT Abuja - Bola Ahmed Tinubu na jagorantar taron majalisar zartaswa ta tarayya (FEC) yanzu haka a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Taron na gudana ne a ɗakin taron majalisar da ke fadar gwamnatin Najeriya yau Talata, 25 ga watan Yuni, 2024.

Taron FEC karkashin Tinubu.
Bola Ahmed Tinubu ya shiga taron majalisar zartarwa a Abuja Hoto: @NGRPresident Asali: Twitter

Kamar yadda Daily Trust ta ruwaito, taron FEC na yau na zuwa ne bayan wanda aka yi kwana biyu ana yi kusan makonni shida da suka gabata.

A zaman FEC na ƙarshe. gwamnatin Bola Tinubu ta amince da ayyuka daban-daban har guda 20.

Waɗanda suka halarci taron da ke gudana yanzu haka sun haɗa da Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume da shugaban ma'aikatan fadar gwamnati Femi Gbajabiamila.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Bugu da ƙari, an tattaro cewa mafi akasarin ministocin Bola Tinubu sun halarci taron FEC a wannan karon.

Idan zaku iya tunawa Shugaba Tinubu ya kaddamar da majalisar ne ranar 28 ga watan Augusta, 2023 kuma ya sauya ranakun taron daga Laraba zuwa Litinin a kowane mako.

Ministan yada labarai, Mohammed Idris, a ranar 16 ga Oktoba, 2023, ya bayyana cewa majalisar za ta rika zama ne idan akwai muhimman batutuwan da za a duba.

"Saboda haka daga yanzu taron FEC ya koma ranakun Laraba kuma ba lallai ne kowane mako za a yi taron ba, idan babu batun da za a tattauna, z a ɗaga zuwa mako na gaba."

Asali: Legit.ng

People are also reading