Gwamnan Zamfara na Shan Sukar Gina Filin Jirgin Saman N62.8b Ana Fama da ’Yan Bindiga
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Jihar Zamfara - Ana cigaba da sukan gwamna Dauda Lawal bisa aniyar gina katafaren filin jirgin sama a jihar.
Gwamna Dauda Lawal zai kashe kudi kimanin Naira biliyan 62.8 domin gina filin jirgin sama a Gusau.
Jaridar Leadership ta ruwaito shahararren dan siyasa a jihar, Dakta Sani Abdullahi Shinkafi na cewa aikin bai dace ba a wannan lokacin.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Tsohon dan takarar gwamna a jihar Zamfara karkashin jam'iyyar AFGA, Dakta Sani Abdullahi Shinkafi ya ce ba buƙatar filin jirgin sama a jihar Zamfara yanzu.
Dakta Sani Abdullahi Shinkafi ya ce abin da mutane ke buƙata shi ne maganin yan bindiga da samar da abubuwan more rayuwa.
Har ila yau, Dakta Shinkafi ya ce ko da za a gina filin jirgin saman bai kamata a ce an ware kudi har N62.8b ba a cewar rahoton Vanguard.
Shinkafi ya ce gwamna Dauda Lawal ya ruɗi ministan harkokin jiragen sama, Festus Keyamo kan cigaba da aikin duk da cewa ba shi ya kamata a kashewa kudin ba.
Aikin filin jirgin saman birnin Gusau dai ya samo asali ne tun a lokacin mulkin gwamna Mahmud Aliyu Shinkafi.
Haka aka cigaba da tafiya karkashin gwamnonin da suka gabata ba tare da an yi aikin ba har wannan lokaci.
A wani rahoton, kun ji cewa mazauna ƙauyen Kukawa a karamar hukumar Maradun a Zamfara sun yi ikirarin sojoji sun masu ruwan bama-bamai a filin idi.
Wani da ya nemi a sakaya sunansa ya ce jirgin ya zo wucewa sai ƴan bindiga suka buɗe masa wuta bisa haka ya saki bam ɗin da ya shafi fararen hula.
Asali: Legit.ng