Home Back

Kwamatin Tsaro na MDD zai yi zaman gaggawa kan harin Isra'ila a Rafah

bbc.com 2024/7/3

Rahoto kai-tsaye

Senegal

Kwamatin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) ya kira ganawar gaggawa a yau Talata domin tattauna harin da Isra'ila ta kai da ya kashe Falasɗinawa kusan 50 a yankin Rafah ranar Lahadi.

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya siffanta harin da "mummunan kuskure," amma ƙasashen duniya na ci gaba da yin tir da harin.

Ƙasar Aljeriya ce ta buƙci a yi ganawar jim kaɗan Babban Sakataren MDD Antonio Guterres ya bi sawun masu yin tir da lamarin.

Ya ce halin da ake ciki a Rafah "tashin hankali ne da ya kamata a dakatar" kuma "babu wani wurin ɓuya a baki ɗayan Zirin Gaza".

Ma'aikatar lafiya ta Gaza ƙarƙashin ikon Hamas ta ce mutum 45 hare-haren na Isra'ila suka kashe ranar Lahadi, yayin da ɗaruruwa suka ji raunukan ƙuna, da karaya, da sauransu.

People are also reading