Home Back

Damuwa kan kashe fararen hula

dw.com 2024/7/5
Burkina Faso | sojoji
Sojojin Burkina Faso

Babban jami'in kula da kare hakkin dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya, Volker Turk ya bayyana damuwa kan kara samun kashe-kashen fararen hula a yankunan kasar Burkina Faso da ke yankin yammacin Afirka. Babban jami'in ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar a wannan Jumma'a, inda ya bukaci cikekken bincike kan abin da yake faruwa a kasar.

Ita dai Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa jami'an tsaron ta Burkina Faso da masu mara musu baya suna halaka fararen hula da dama da suke zargi da hannu cikin tashe-tahsen hankula da kasar take fuskanta.

People are also reading