Rikicin makiyaya da manoma ya hallaka mutane 21 a Najeriya
Rikicin makiyaya da manoma ya yi sanadiyyar mutuwar kimanin mutane 21 a jihar Kogi da ke tsakiyar Najeriya, kamar yadda shugaban karamar hukumar Omala Mr Edibo Ameh Mark ya tabbatarwa kamfanin dillancin labarai na Reuters.
Mr Mark ya ce makiyayan sun yi ramuwar gayya ne a daren Alhamis, bayan kashe musu mutane 6 kwanaki 3 da suka gabata, kuma a Juma'ar nan aka yi jana'izar mutane 21 din da suka mutu.
Rikicin makiyaya da manoma dai ba sabon abu bane a Najeriya musamman a yankin arewaci, wanda ya jima yana janyo asarar rayukan mutane da dabbobi.