Home Back

Hajj 2024: Bayan Mutuwar Tawakaltu, Wani Alhajin Najeriya Ya Mutu Yana Ibada a Saudiya

legit.ng 2024/7/1
  • Wani Alhaji daga jihar Kebbi, Muhammad Suleman ya rasu bayan ya yi fama da gajeruwar rashin lafiya a birnin Makka na kasar Saudiyya
  • Marigayin ya rasu ne a ranar Lahadi kuma an yi sallar jana’izarsa a masallacin Harami (Ka’aba) tare da yi masa sutura
  • Rasuwar Muhammad ta kara adadin yawan alhazan Najeriya da suka rasu zuwa biyu, bayan mutuwar Hajiya Tawakaltu Alako

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Makka, Saudiya - Wani Alhajin Najeriya da ke gudanar da aikin Hajji ya rasu a kasar Saudiyya. An ce marigayin dan asalin jihar Kebbi ne.

Shugaban hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kebbi, Faruku Aliyu-Enabo ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai ranar Lahadi.

Dan Najeriya ya rasu wajen aikin Hajji a Saudiya
Wani dan jihar Kebbi ya rasu a Saudiya yayin da ya ke gudanar da aikin Hajji. Hoto: @MoHU_En Asali: Twitter

SaudiyaAlhajin Najeriya ya rasu a Saudiya

Jaridar Premium Times ta ruwaito cewa marigayin Muhammad Suleman, ya rasu ne a ranar Lahadi bayan gajeruwar jinya a garin Makkah.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hakan ya biyo bayan rasuwar wata Hajiya mai suna Tawakaltu Alako wadda ita ma ‘yar asalin jihar Kebbi ce.

Alako ta rasu ne a ranar Asabar bayan ta yanke jiki ta fadi otal din da ta ke zama a Makkah.

Aliyu-Enabo ya bayyana cewa an yi jana’izar Suleman kamar yadda addinin Musulunci ya tanada, in ji rahoton jaridar The Cable.

Gwamnatin Kebbi ta mika sakon ta'aziyya

“Marigayin ya rasu ne a ranar Lahadi bayan ya yi fama da gajeruwar rashin lafiya kuma an yi sallar jana’izarsa a masallacin Harami (Ka’aba).
“A madadin gwamnatin jihar Kebbi, ina mika sakon ta’aziyyarmu ga iyalansa, alhazan Kebbi da daukacin jihar baki daya.
"Muna rokon Allah Madaukakin Sarki da ya gafarta masa kurakuransa, ya kuma jikansa da rayukan dukkan Musulmin da suka rasu."

- In ji Aliyu-Enabo.

An nada Amirul Hajji na Kano

A wani labarin, mun ruwaito cewa gwamnan jihar Kano, Abba Yusuf ya nada sabon Amirul Hajji da zai jagoranci maniyyatan Kano zuwa aikin Hajjin bana a Saudiya.

Abba ya nada mataimakin gwamnan jihar, Aminu Abdulsalam a matsayin Amirul Hajj na Kano a bana yayin da alhazan jihar za samu kyautar $500 kowanne.

Asali: Legit.ng

People are also reading