Home Back

“Da Kun Yi Koyi da Magabatanku”: Farfesa Ya Shawarci Aminu Ado da Sanusi II

legit.ng 2024/10/5
  • Farfesa Umar Labdo ya yi karin haske kan dambarwar sarautar Kano inda ya ba masu rigimar shawara game da shawo kan matsalar
  • Farfesan ya ce tun farko ya kamata Sanusi II da Aminu Ado su yi koyi da Muhammadu Sanusi I bayan tube shi a sarauta
  • Labdo ya ce wannan rigimar cikin gida ne wanda 'yan siyasa ke kara hura wutar domin biyan bukatar kansu a jihar

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Yayin da ake ta dambarwa kan sarautar Kano, Farfesa Umar Labdo ya ba da shawarar kawo karshen rigimar.

Umar Labdo ya ce da ace Sanusi II da Aminu Ado sun yi koyi da magabatansu da wannan rigima ba ta taso ba.

Farfesan ya bayyana haka a cikin wata hira da ya yi da jaridar Vanguard inda ya bayyana damuwa kan matsalar.

Labdo ya ce ya kamata tun farko sarakunan sun yi koyi kakan Sanusi II wanda ake kira Muhammadu Sanusi I bayan tube shi a Jamhuriya ta daya.

Ya ce gwamnan wancan lokaci, Abubakar Rimi ya yi kokarin dawo da shi sarauta amma yaki amincewa inda ya ce ba zai yi gardama da dan uwansa ba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

People are also reading