Home Back

Ganduje Ya Ƙara Rusa Ƴan Adawa, Manyan Jiga-Jigai da Dubban Mambobi Sun Koma APC

legit.ng 2024/7/5
  • Mambobin babbar jam'iyyar adawa PDP sama da 4,000 sun tattara kayansu sun koma jam'iyyar APC mai mulki a jihar Benuwai
  • Gwamna Hyacinth Alia ne ya karɓe su da kansa a wani taro da aka shirya lokacin da yake zagayen godiya ga al'ummar jihar da suka zaɓe shi
  • A jawabin da ya yi, ya cegwamnatinsa za ta yi duk mai yiwuwa wajen samar da tsaro a faɗin jihar domin mutane su ci gaba da harkkinsu babu fargaba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Benue - Yayin da manyan jam'iyyu ke ci gaba da shirye-shiryen tunkarar babban zaɓen.2027, jam'iyyar APC mai mulki ta samu ƙaruwa a jihar Benuwai.

Dubban mambobin jam'iyyar PDP waɗanda suka kai kimanin 4,450 sun watsr da tafiyar laima, sun koma jam'iyyar APC ranar Talata.

Gwamna Alia na jihar Benuwai.
Gwamnan Benuwai ya karbi dubannin mambobin PDP da suka sauya sheka zuwa APC Hoto: Hyacinth Alia Asali: Facebook

Kamar yadda Aminiya ta ruwaito, dubban masu sauya sheƙar sun fito ne daga kananan hukumomi 5 da suka haɗa da Katsina-Ala, Ukum, Logo, Kwande da Ushongo.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamna Hyacinth Alia na jihar Benuwai ne ya karɓi masu sauya shekar a wnai taro da aka shirya yayin da yake zagayen godiya ga jama'a da suka zaɓe shi a 2023.

Da yake jawabin a taron maraba da masu sauya sheƙar, Gwamna Alia ya miƙa godiya ga mutanen jihar bisa yadda suka amince suka zaɓe shi duk da cewa shi sabo ne a siyasa.

Alia ya kuma kara jaddada kudirinsa na mayar da ƴan gudun hijurar da hare-haren ƴan bindiga ya raba da mahallansu zuwa garuruwansu.

Haka nan kuma gwamnan ya nuna takaicinsa kan yadda ƴan bindiga suka addabi yankin Sankera, cibiyar noman doya a jihar da ke Arewa ta Tsskiya.

Ya bayyana cewa gwamnatinsa ba za ta yi ƙasa a guiwa ba wajen tabbatar da tsaro da kwanciyar hankala a faɗin jihar.

Sai dai ya ja hankalin jama'a cewa aikin samar da tsaro ba na gwamnati bane ita kaɗai, ya zama filas kowa ya bayar da gudummuwa daidai gwargwado.

Rikicin Kano: NNPP ta caccaki APC

A wani rahoton kuma Jam'iyyar NNPP mai kayan marmari ta zargi APC da yunƙurin kwace mulki ta kowane hali a jihar Kano da ke Arewa maso Yamma.

A wata sanarwa da kakakin NNPP na ƙasa ya fitar, jam'iyyar ta tona yadda APC ke amfani da shari'a da jami'an tsaro don tayar da zaune tsaye a jihar.

Asali: Legit.ng

People are also reading