Home Back

Afirka ta Kudu: Za a zabi shugaban kasa

dw.com 2024/10/6
Hoto: Kyodo/picture alliance

A karshen watan Mayu aka gudanar da zaben yan majalisar wanda a karon farko tun bayan zuwan mulkin demokaradiyya a kasar a shekara ta 1994. Jam'iyyar ANC mai mulki ta rasa rinjaye a majalisar wanda sai ta nemi kawance a yanzu da sauran jam'iyyun domin kafa gwamnati. Kamar yadda kundin tsarin mulkin na Afirka ta Kudu, ya tanada, dole ne a zabi shugaban majalisar, da mataimakinsa da kuma shugaban kasar a lokacin zaman majalisa na farko bayan zaben. Shugaban kasar na yanzu Cyril Ramaphosa, mai shekaru 71, na neman wa'adi na biyu. Sai dai kawo yanzu babu tabbas, ko zai wuce amma dai kawo yanzu  jam'iyyarsa na tattaunawa da sauran jam'iyyun siyasa don kafa gwamnatin.

People are also reading