Gwamnatin Tarayya Za Ta Karawa Ma’aikatan Lafiya Albashi, Ministan Tinubu Ya Yi Bayani
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida
Abuja - Ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Ali Pate, ya yi albishir ga likitocin Najeriya, inda ya ce gwamnati za ta kara musu albashi nan ba da dadewa ba.
Da aka tambaye shi ko ma'aikatan lafiya za su samu karin albashi mai tsoka, Ali Pate ya ce nan gaba kadan ma'aikata za su ji labarin karin albashin daga gwamnati.
Ministan ya bayyana hakan ne a cikin wani shiri na musamman a gidan talabijin din Channels kan bikin cikar shugaban kasa Bola Tinubu shekara daya a mulki.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
A tsawon shekaru, kwararru a fannin kiwon lafiya a Najeriya sun yi ta korafin karancin albashi da kuma rashin biyan su alawus alawus da sauransu.
Sakamakon rashin samun albashi mai tsoka, wasu da dama daga cikin ma'aikatan lafiya sun yi kaura zuwa ketare, lamarin da ya haifar karancin likitoci a Najeriya.
Da yake magana game da matsalar fannin kiwon lafiya, ministan lafiya ya ce gwamnatin Tinubu ta dauki wasu muhimman matakai na magance wadannan matsalolin.
Sakamakon aiwatar da wadannan matakan, ministan ya ce wasu kwararrun ma'aikatan da suka bar Najeriya zuwa Turai a yanzu suna kokarin dawowa kasar.
Ali Pate ya ce gwamnati ta dauki ma'aikatan jiya, ungozoma da likitoci 2,497 aiki tare da tura su zuwa cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko a cikin shekara daya.
Kalli tattaunawar a nan kasa:
A wani labarin, mun ruwaito cewa wani alhajin Najeriya daga jihar Kebbi, Muhammad Suleman ya rasu bayan ya yi fama da gajeruwar rashin lafiya a kasar Saudiya.
Marigayin na daga cikin maniyyatan Najeriya da suka je Saudiya domin sauke farali a aikin Hajji na bana, kuma an gudanar da jana'izarsa tare da binne shi a Makkah.
Asali: Legit.ng