Home Back

Sarautar Kano: Abba Kabir Ya Magantu Kan Sahihancin Samun Takarda Daga Kotu

legit.ng 2024/6/26
  • Gwamnatin jihar Kano ta yi fatali da jita-jitar samun takardar umarnin kotu kan tube sarakuna biyar da Gwamna Abba Kabir ya yi
  • Kwamishinan Shari'a a Kano, Haruna Isah Dederi shi ya bayyana haka inda ya ce har yanzu basu samu takardar a hannunsu ba kamar yadda ake yadawa
  • Dederi ya bukaci yan jihar su kwantar da hankalinsu inda ya ce babu wata takarda daga kotu da aka mikawa gwamnatin Kano

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Gwamnatin jihar Kano ta yi martani kan sahihancin takardar kotu da ke haramta tube sarakuna biyar a jihar.

Gwamnatin ta ce har yanzu ba ta samu wata takarda musamman da ke haramta abin da gwamnan ya aikata ba kan kujerar sarautar jihar.

Abba Kabir ya yi martani kan umarnin kotu game da sarautar Kano
Gwamnatin Kano ta musanta samun wata takarda daga kotu. Hoton: @Kyusufabba, @iamMacAfeez. Asali: Twitter

Kano: Gwamnati ta musanta samun takardar kotu

Kwamishinan shari'a, Barista Haruna Isah Dederi shi ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da aka yada a shafin X.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Dederi ya ce har zuwa wannan lokaci babu wata takarda da gwamnatin Kano ta samu kan wannan mataki da ake magana.

Ya bayyana cewa shi ne mutum na farko da ya kamata ya samu takardar a matsayinsa na kwamishinan Shari'a amma bai ga komai ba.

"Ina amfani da wannan dama domin fadawa mutanenmu gaskiyar lamari kan takardar da ke yawo a kafafen sadarwa."
"A iya sani na babu wata takarda ta umarnin kotu da aka damkawa gwamnatin Kano kamar yadda ake yadawa."
"Idan har za a ba da wani umarni to dole ta hannuna za a mika a matsayina na kwamishinan shari'a."

- Haruna Dederi

Kwamishina ya bukaci a kwantar da hankali

Kwamishinan ya ce a doka kotu bata ba da umarni kan abin da aka riga aka kammala shi inda ya ce har yanzu suna dakon jiran takardar daga kotu.

Ya bukaci al'ummar jihar Kano su kwantar da hankulansu su bar jita-jita kan abin da ake yadawa a kafafen sadarwa da ba a dogara da su ba.

Kano: Ribadu ya yi barazanar shiga kotu

Kun ji cewa, Mallam Nuhu Ribadu ya yi barazanar maka mataimakin gwamnan Kano, Abdulsalam Aminu Gwarzo a gaban kotu kan bata masa suna.

Ribadu ya dauki wannan matakin ne bayan Gwarzo ya zarge shi da hannu a rikicin sarautar jihar Kano.

Asali: Legit.ng

People are also reading