Home Back

An Tsaurara Tsaro Bayan Fara Shari’a Kan Rikicin Masarautar Kano

leadership.ng 2024/7/4
An Tsaurara Tsaro Bayan Fara Shari’a Kan Rikicin Masarautar Kano

An tsauraran matakan tsaro a harabar babbar kotun tarayya da ke zamanta a kan titin Court Road da ke Jihar Kano, yayin da aka fara sauraren karar rikicin masarautar jihar.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, ‘yansanda da jami’an hukumar DSS, sun girke motocinsu a kan hanya tare da hana zirga-zirga.

Masu ababen hawa na bin hanyar Gyadi-Gyadi ko Zoo Road domin kaucewa cunkoso.

Yajin aikin da aka yi na kwanaki biyu ne, ya hana zaman babbar kotun, kan batun dawo da Sarki Sanusi II a matsayin Sarkin Kano.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa wata babbar kotun tarayya da ke Kano ta bayar da umarnin dakatar da gwamnatin Jihar Kano daga aiwatar da dokar da ta rushe masarautun jihar.

Mai shari’a Mohammed Liman ya bayar da wannan umarni ne, bayan da Sarkin Dawaki Babba, Alhaji Aminu Babba Dan Agundi ya shigar da kara.

An shirya fara zaman kotun da misalin karfe 10 na safe, a ranar Alhamis, amma aka sauya lokaci.

People are also reading