Home Back

JUNE 12: Uba Sani ya yi wa fursinoni 110 afuwa a Kaduna

premiumtimesng.com 2024/7/3
JUNE 12: Uba Sani ya yi wa fursinoni 110 afuwa a Kaduna

Domin murnar zagayowar ranar Dimokuraɗiyya a Najeriya gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani ya bayar da umarnin a saki fursunoni 110 daga gidan gyaran hali da ke jihar.

Gwamna Sani ya yi haka ne somin taɓi na wani a zaman wani bangare na bikin ranar dimokradiyya na bana da kuma murnar cika shekara guda a kan karagar mulki.

Gwamna Sani tare sa wasu manyan jami’an gwamnati sun ziyarci gidan gyaran hali na jihar Kaduna tare da fitattacen lauya Femi Falana (SAN), inda ya bayyana bukatar a yi garambawul a gidajen gyaran hali da ke jihar Kaduna.

Ya kara da cewa matakin da ya dauka na sakin fursunonin 110 ya je daidai da ikon da ya ke da shi a karkashin tanadin sashe na 212 na kundin tsarin mulkin Najeriya na shekarar 1999.

A nasa bangaren, Falana ya yaba wa Gwamna Sani bisa afuwar da ya yi wa fursunonin.

Ya kuma yi kira ga manyan alkalan jihohi da su ba da umarnin a rinka gudanar da bincike lokaci zuwa lokaci a ofisoshin ‘yan sanda a jihohinsu don duba batun tsare mutane ba bisa ka’ida ba, ya kuma yi kira ga gwamnonin jihohin kasar da su ba da fifiko wajen gyaran cibiyoyin gyaran halin da ke jihohinsu.

An dai gina gidan gyaran hali na Kaduna a shekarar 1915 ne, wanda zai iya daukar fursunoni 500.

Amma a halin yanzu, cibiyar tana da fursunoni sama da 3,000 a cikin ta, yayin da wadanda ke jiran a yanke musu hukunci suke birjik a gidan batare da an waiwaye su.

People are also reading