Home Back

Jigo a APC Ya Wanke Tinubu Daga Zargi Kan Wuyar da Ake Sha a Najeriya

legit.ng 2024/6/18
  • Wani jigo a jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya ya fito ya wanke shugaban ƙasa Bola Tinubu daga zargi kan halin matsin da ake ciki a Najeriya
  • Ismaeel Ahmed ya bayyana cewa bai kamata a ɗora alhaki kan Shugaba Tinubu ba saboda taɓarɓarewar da tattalin arziƙin ƙasar nan ya yi ba
  • Ya bayyana cewa matakan da shugaban ƙasar ya ɗauka sun zama wajibi ne domin fargaɗo da tattalin arziƙin ƙasar nan daga doguwar sumar da ya yi

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Jigo a jam'iyyar APC, Ismaeel Ahmed, ya wanke shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu kan taɓarɓarewar da tattalin arziƙin ƙasar nan ya yi.

Ismaeel ya bayyana cewa bai kamata a ɗora alhakin halin da ƙasar nan ke ciki ba a kan shugaban ƙasar duk da yanayin tsadar rayuwa da hauhawar farashin kayayyaki da ƴan Najeriya ke fama da su.

Jigo a APC ya wanke Tinubu daga zargi
Tun bayan hawan Tinubu kan mulki rayuwa ta yi tsada a Najeriya Hoto: @DOlusegun Asali: Facebook

Ismaeel Ahmed ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da tashar Channels tv a shirinsu na 'Politics Today' ranar Talata.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jigo a APC ya goyi bayan Tinubu

Ya bayyana cewa matakai masu tsauri da gwamnati mai ci ta ɗauka sun zama wajibi ne domin farfaɗo da tattalin arziƙin ƙasar nan.

"An ɗauki tsauraran matakai. Babu ɗaya daga cikin waɗannan matakan da ba a yi alƙawari ba a lokacin yakin neman zaɓe ba, ba wai shugaban ƙasa Bola Tinubu kaɗai ba, har ma da sauran ƴan takara."
"Muna cikin wani yanayi da ya kamata al’amura su daidaita. Shugaban ƙasa ya ɗauki tsauraran matakai, abin ba daɗi, dukkanmu muna ji a jikinmu, amma ba zan ce shugaban ƙasa za a ɗorawa laifi ba."

- Ismaeel Ahmed

Jigon na APC ya ce kafin zaɓen shugaban kasa na ranar 25 ga watan Fabrairun 2023, ƴan takarar jam’iyyar Labour Party (LP), Peter Obi da takwaransa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar sun yi alƙawarin kawo ƙarshen tallafin man fetur.

ACF ta soki Tinubu

A wani labarin kuma, kun ji cewa ƙungiyar tuntuɓa ta Arewa (ACF) ta ɗora alhakin halin matsin tattalin arziƙin da ake fama da shi a ƙasar nan kan shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu.

Ƙungiyar ta bayyana cewa wasu daga cikin manufofin da gwamnatin Tinubu ta kawo ne silar jefa ƴan Najeriya cikin halin wuya a ƙasar nan.

Asali: Legit.ng

People are also reading