Home Back

Tsadar Rayuwa: Gwamnan Arewa Ya Yi Abu 1 da Ya Faranta Ran Ma’aikatan Jiharsa

legit.ng 2024/5/20
  • Kwamishinan yada labarai na jihar Jigawa, Sagir Musa ya ce gwamnatin jihar ta sake daukar matakin saukaka wa rayuwar ma'aikatan jihar
  • Sagir Musa ya bayyana ce jihar ta ware Naira biliyan 1.1 domi sayen kayan abinci wanda za ta sayarwa ma'akata kan farashi mai rahusa
  • Hakazalika, kwamishinan ya ce akwai shaguna da aka bude a dukkanin kananan hukumomin jihar inda ma'aikata za su karbi abinci a bashi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Jihar Jigawa - Gwamnatin jihar Jigawa ta ware Naira biliyan 1.1 domi siyan karin kayan abinci na gaggawa da za a sayarwa ma'aikatan jihar.

Gwamnatin Jigawa za ta kashe N1.1bn domin tallafawa ma'aikatan jihar
A cewar gwamnati, ma'aikatan Jigawa za su rika sayen abinci a farashi mai rahusa. Hoto: @uanamadi Asali: Facebook

Kwamishinan yada labarai, matasa, wasanni da al’adu, Sagir Musa ne ya bayyana haka yayin da yake zantawa da manema labarai a jiya Alhamis.

Kayan abinci da za aba ma'aikata

Sagir Musa ya ce gwamnati ta cimma wannan matsayar ne a taron majalisar zartarwa da ya gudana a ranar Litinin da nufin saukakawa ma'aikatan kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kayayyakin da za a siya sun hada da buhunan shinkafa 12,000 da katon 15,000 na taliya, wanda za a sayarwa ma’aikatan gwamnatin kan farashi mai rahusa.

Ya ce siyan kayan abincin na cikin shirin gwamnatin jihar na samar da shaguna na hadin gwiwa a dukkan kananan hukumomi 27 na jihar.

"Ma'aikata za su iya karbar bashi" - Musa

Jaridar Leadership ta rahoto kwamishinan na nuni da cewa za ayi amfani da shagunan a matsayin wuraren da ma'aikatan jihar za su rika sayen kayan abinci a farashi mai rahusa.

Sagiru ya ce tuni aka samar da hanyoyin kafawa da sarrafa shagunan hadin gwiwar inda ma’aikata za su iya karbar kayan abinci a kan bashi da kuma biyan kudin kadan-kadan.

Kwamishinan ya kara da cewa an kashe N2.8bn a shirin ciyar da al'uma abinci a watan Ramadan na bana.

An kara wa ma'aikata albashi a Jigawa

A wani labarin, Legit Hausa ta ruwaito cewa gwamnatin jihar Jigawa ta yi karin albashi na Naira 30,000 ga ma'aikatan jihar wanda zai yi aiki na watanni uku.

A cewar gwamnatin jihar, an yi karin albashin ne domin rage wa ma'aikatan radadin tsadar rayuwa da kasar ke fuskanta sakamakon janye tallafin man fetur.

Asali: Legit.ng

People are also reading