Home Back

YUNWA DA TALAUCI: Mazauna Abuja sun fasa gidan ajiyar kayan tallafi na NEMA, sun daka wasoson kayan abinci

premiumtimesng.com 2024/4/29
YUNWA DA TALAUCI: Mazauna Abuja sun fasa gidan ajiyar kayan tallafi na NEMA, sun daka wasoson kayan abinci

Wasu mazauna garin Karimo da ke gundumar Babban Birnin Tarayya, FCT Abuja, sun fasa katafaren rumbun ajiyar kayan tallafin abinci, suka daka wasoson abin da kowa zai iya ɗiba.

Lamarin ya faru a ranar Lahadi, wajen 7 na safe, har zuwa 9 na safe mutane na jidar kayan abinci.

An fasa rumbun ajiyar kayan abincin ne a daidai lokacin da raɗaɗin tsadar rayuwa da tsadar kayan abinci ke nuƙurƙusar ‘yan Najeriya.

A wasu garuruwa kuma, ana tare motocin da ke ɗauke da lodin kayan abinci ne ana wasoso ƙarƙaf.

Matsalar tsadar rayuwa dai ta samo asali tun bayan cire tallafin fetur da Shugaba Bola Tinubu ya yi, tun a ranar 29 ga Mayu, 2023, ranar da aka rantsar da shi.

Ko cikin wannan makon ma sai da Tinubu ya ce ‘cire tallafin fetur ya zama ciwon ido, sai dai a yi haƙuri kawai.’

Rahotanni sun tabbatar da cewa ko a lokacin kullen korona sai da mabuƙata suka fasa rumbun ajiyar kayan abincin a cikin 2020.

Hakan na nuna cewa ba wannan ne karo na farko da hasalallu su ka fara fasa rumbun ajiyar kayan tallafin ba.

Jami’an ‘yan sanda sun shaida wa Daily Trust cewa jami’an su sun isa wurin, kuma komai ya koma kamar kullum.

Cikin makon jiya ne Ƙungiyar Ƙwadago ta Ƙasa ta yi zanga-zangar lumana a faɗin ƙasar nan, domin nuna damuwa dangane da mawuyacin halin tsadar rayuwa da tsadar kayan abinci da ake fama da su a ƙasar nan.

 
People are also reading