'Yan takarar shugaban kasar Mauritania na karkare yakin zabe
A Juma'ar nan ce 'yan takarar shugaban kasa a ke karkare gamgamin yakin tallata manufofinsu, domin tunkarar zaben da za a gudanar a gobe Asabar.
Karin bayani:Mauritania
To sai dai shugaban kasar Mohamed Ould Cheikh El Ghazouani ya ce babu makawa shi zai sake lashe zaben, domin samun wa'adin mulki na biyu.
'Yan takara bakwai ne ciki har da shugaba mai ci ke takarar zaben, a wannan kasa mai fama da hare-haren ta'addancin masu ikirarin jihadi.