Home Back

An zargi Jami’in Soja da barazanar harbe wasu jami’an gidan gyaran hali a Kano

dalafmkano.com 5 days ago

Rahotanni daga jihar Kano sun bayyana yadda aka zargi wani Soja, da ya yi barazanar harbe wasu jamipan gidan ajiya da gyaran hali a jihar.

Al’amarin ya faru ne a harabar kotunan majistret da ke unguwar Nomansland a Kano, inda sojan ya je bakin ƙofar ɗakin da ake ajiye waɗanda ake tuhuma ya bai wa wani wanda ake tuhuma kudi, ba tare da sanin jami’an gidan gyaran halin ba.

Yayin da jami’an gidan gyaran halin suka yi masa magana sai ya bayyana musu cewar shi fa Soja ne, kuma idan ba su bishi a hankali ba zai fisge bindigar su ya harbe su a wajen.

Sai dai a lokacin da jami’an gidan gyaran halin suka fuskanci barazanar sai suka damƙe sojan inda suka miƙa shi caji ofishin ƴan sanda na Nomansland, kamar yadda shaidar gani da ido Barista Lawan Lawan Usman ya shaidawa Dala FM Kano.

Wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’il ya tunduɓi mai magana da yawun hukumar gidajen ajiya da gyaran hali ta jihar Kano SC Musbahu Lawan Ƙofar Nassarawa, sai dai ya ce za su binciki yadda batun ya ke.

People are also reading