Home Back

Yiwuwar shiga yajin aikin gama gari a Kenya

dw.com 2024/7/3
Hoto: LUIS TATO/AFP/Getty Images

Wannan mataki na zuwa ne bayan zanga-zangar da akasarinsu matasa suka yi a wannan makon a fadin kasar Kenya.

Wata sanarwa da masu zanga-zangar suka yi ta yadawa ta yanar gizo, na kira ga daukacin al'ummar kasar ta Kenya da su fito kwansu da kwakwatarsu dopn nuna adawa da makain gwamnatin Nairobi, ta hanyar shiga yakin aikin na gama gari.

Gwamnatin Shugaba William Ruto ta kasar da ke fama da karancin kudade dai ta amince a ranar Talatar da ta gabata cewa za ta dubi yiwuwar yin gyara-gyare ga tsarin harajin, bayan arangamar da ta wakana a tsakanin wasu daruruwan matasa da jami'an 'yan sanda a Nairobi babban birnin kasar.

Sai dai kuma alamu na nuna cewa gwamnatin ta Kenya, za ta ci gaba da wasu kare-kare a kan wasu haraje-haraje, a kokarinta na rage yawan basuka da take karbowa daga ketare domin matsalolin cikin gida.

People are also reading